Mahaifin Ummu Habiba ya rasu, kuma ta kasance taji hanin yin takaba sama da Uku sai akan miji, sai ta so tabbatar da aiki da wannan Hadisi, sai ta nemi akawo mata turare wanda yake an cudanya shi da wani abu rawaya, sai ta shafi dantsenta, kuma tayi bayanin abinda ya sanya ta ta saka Turaren kuma shi cewa ita taji Annabi yana cewa: "Bai halatta ga Mace ba tayi Imani da Allah da kuma ranar lahira tayi Takabar mutuwa sama da da uku, sai dai in akan Miji ne: Wata hudu da kwana gom"