An rawaito daga Nana Aisha -Allah ya yarda da ita- daga Annabi: "Idan dayanku yayi gyagyadi a cikin Sallah to ya kwanta har sai baccin ya tafi, saboda dayanku idan yayi Sallah yana gyangyadi bai san watakila yaje yana neman Istigfari sai ya zagi kansa (Maimakon haka)" Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi