Annabi ya jinkirta fitowa zuwa ga sallar issha'i har dare yayi ,mata da yara sun kwanta bacci,wanda basu da jumurin jira mai tsawo,sai Umar Dan Khaddab ya zo wajensa yace: sallah,mata da yara sun yi bacci. sai Manzo tsira da aminci ya fito daga gidansa zuwa masallaci kansa yana digar da ruwan wanka yana bayyana cewa mafi kyawun liokacin sallar issha'i shine a jinkirta ta.ba don gudun wahalar jiran lokacin ba:ba don kan in matsawa al'umma ta ba da na umarce su da wannan sallar a irin wannan lokacin