Manzon Allah SAW ya Kasance yana sanya riguna biyu na Qarfe; saboda kare kansa daga sukar Abokan gaba a yaqin Uhudu sai ya tashi ya fuskanci wani Dutse; don ya hau kansa bai iya hawa ba, sai Xalha -Allah ya yarda da shi- ya zo ya sunkuya kasan manzon allah SAW sai ya hau kansa har ya iya hawa kan Dutsen, sai manzon Allah SAW ya ce: "Ta wajaba ga Xalha" ai lallai cewa xalha da wannan aikin nasa ya tabbatarwa da kansa da wannan aiki na yau ya samu al-janna, kuma ya cancanceta da wannan aikin