Yayin da Allah ya halicci nAnnabi Adam a cikin Aljanna kuma ya tsara Surarsa, sai ya barshi wani lokaci bai busa masa rai ba, sai Iblis ya rika kewaye gefensa, yana Kallons; don yasan wane abu ne wannan, yayin da ya ga cikin sa babu komai, sai yasan cewa shi Halitta ce Mai rauni da ba zata iya juriya ba wajen Waswasinsa, ko ya san cewa shi zai iya zuwa da zunubi ta hanyar cikinsa, saboda haka aka zo masa ta hanyar Bishiya, ko kuma ya kasance ya sani cewa yasan Halitta mai ciki rarrauna ce, kuma wasu Mutane sun kasa gane fadinsa: "Cikin Al-janna" tare da cewa abunda ya zo cewa Allah ya halicci Annabi Adam daga bangarorin Kasa, sai ka amsa musu da cewa shi an barshi a haka ne har tsawon lokaci har kirarsa ta zamanto yadda zata iya Karbar Rai, sannan aka dauke shi zuwa Al-janna kuma aka busa Masa rai a cikinta.