An rawaito daga Al-Sa'ib Bn Yazid -Allah ya yarda da shi- yace: "Yayin da Annabi SAW ya iso Madina- daga yakin Tabuka Mutane sun tare sai na tare shi tare da Yara, kuma a cikin wata Riwayar ya ce:"Mun tafi mu taro Annabi SAW tare da Yara a Thaniyat Al-Wadaa" Ingantacce ne - Buhari ne ya rawaito shi - Abu Daud Ya Rawaito shi
explain-icon

Bayani

Ma'anar hadisin: - Al-Saib bin Yazid - Allah ya yarda da shi - ya ce Annabi - SAW- lokacin da ya zo daga yaqin Tabuka, mutane - waxanda suka bari daga yaqin neman gafara da wasunsu - suka tafi gidan bankwana don karvar sa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - lokacin da Dawowarsa. Al-Saib bin Yazid ya fita tare da yaran Madina don ganawa da Annabi - SAW