explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa imani cikakke ba ya tabbata ga wani daga musulmai har sai ya so wa ɗan'uwansa abinda yake sowa kansa na ayyukan ɗa'a da nau'ukan alkairai a addini da rayuwa, kuma ya ki abinda yake ki ga kansa, idan ya ga wata tawaya ga ɗan'uwansa musulmi a addininsa, to ya yi kokari a cikin gyarata, idan ya ga wani alheri a cikinsa to ya daidaita shi ya taimake shi, ya yi masa nasiha a al'amarin Addininsa da duniyarsa.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Wajabcin so wa mutum ga ɗan'uwansa abinda yake so wa kansa; domin kore imani ga wanda ba ya son abinda yake so ga ɗan'uwansa yana nuni akan wajabcin hakan.
  • 'Yan uwantaka a tafarkin Allah sama take akan 'yan uwantaka ta nasaba, to hakkinta shi ne mafi wajaba.
  • Haramcin dukkan abinda yake kore wannan soyayyar na maganganu da ayyuka, kamar algus da raɗa da hassada da ta'addanci akan ran musulmi ko dukiyarsa ko mutuncinsa.
  • Yin anfani da wasu daga lafuzza masu kwaɗaitarwa akan yin aiki; saboda faɗinsa: "Ga ɗan'uwansa".
  • Karmani - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: Kuma yana daga cikin imani ya ki wa ɗan'uwansa abinda yake ki wa kansa na sharri, amma bai ambace shi ba; domin son abu mai lazimtar kin kishiyarsa ne , to hakan ya isu akan barin fadinsa.