Bilal ya zo wajen Annabi da Dabino Biryani mai kyau, sai Annabi yayi mamakin kyawun kansa kuma ya ce: Daga ina wannan? sai Bilal ya ce: ina da wani Dabino ne, sai na bada kwano biyu na mara kyau aka bani kwano daya na wannan mai kyau, don ya kasance na kawowa Annanbi daga cikinsa, sai hakan ya girmama ga Annabi kuma yayi kash da hakan, domin hakan Sabo ne a wajensa kuma shi ne Mafi girman Musibu, kuma ya ce: wannan aikin naka, shi ne tsantsan Riba wacce aka haramta, to kada kayi hakan, sai dai idan kanaso sai ka canza mara kyawun da kudi ta hanyar siyarwa, sannan kudin sai ka siyi Dabinon da shi mai kyau, to wannan hanya ita halas ce kana iya yinta, don nisantar fadawa cikin haramun. "Taisir Allam Sharhin Umdatu Al'ahkam" (Shafi/568)