Ummu Sulai 'Yar Madina -Allah ya yarda da ita- ta zo wajen Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- don ta tambaye shi,kasancewar tambayar na da alaka da matunci,akan ji kunyar fada,shi ne ta fara gabatar da yan kalmomin don yin shimfida ga tambayar ta. Sai tace: Allah Madukaki shi ne Gaskiya,bai hana ambaton gaskiya,in dai akwai wani amfani cikin tambayar,bayan Ummu Sulaim ta gabatar da wannan shimfida,sai ta fadi tambayarta kai tsaye,tace:shin mace zata yi wanka in tayi mafarki ana saduwa da ita?Sai Annabi tsira da aminci yace,za ta yi wanka indai har ta ga mani.