Aliyu Dan Abu Dalib-Allah ya yarda da shi- daga Annabi cewa ya Auri 'Diyar Baffansa Hamza. sai ya bashi labari cewa bata halatta a gareshi ba, domin ita 'Diyar Dan uwansa ce da aka shayar da su tare, kuma cewa shi da Baffan sa dukkansu Suwaiba ta shayar da su kuma baiwa ce ta Abu Laha, sai ya zamanto Dan uwansa ta wajen Shayarwa, kuma ya zamanto Baffan 'Diyarsa, kuma ya haramta ta hanyar shayarwa, duk abunda haihuwa ta haramta.