Ummu Salamah, Allah ya yarda da ita, ta ce wa Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: Shin ina da wani lada a ciki na ciyar da ‘ya’yana daga Abu Salamah kuma na isar musu, kuma ban bari su watse a cikin neman guzuri ba? Ko kuwa babu wani sakamako a wurina saboda na yi ta ne da tausayi saboda 'ya'yana ne? Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya gaya mata cewa za a ba ta ladan ciyarwa a kan su.