Abdullahi Dan Umar -Allah ya yarda dasu- yana bada labarin cewa Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi- ya yi rabon ganimar yaki ya bawa doki kaso biyu, mutum kuma kaso daya, kuma alkur'ani yayi nuni da haka inda Allah Madaukaki ke cewa:[Ina rantsuwa da dawaki masu kai hari da asuba, sai su tayar da kura game da shi, sai su shi tsakanin makiya da ita kurar] {al'adiyat 3-5}. Wannan na nuni ga muhimmancin doki a fagen daga. Annabi tsira da amincin Allah yace: [ Akwai alheri ga makwankwadar doki har zuwab ranar kiyama]